Asabar 6 Yuni 2026 - 16:47
Jajircewar Imam Kazim (AS) Ita Ce Silar Tsayuwar Mazhabar Shi'a Cikin Tarihi

Hauza/ Memba na Ƙungiyar Malaman Gwagwarmaya (Jami'at-e Ruhaniyat-e Mubarez) ya bayyana cewa boyayyen ƙoƙari da sadaukarwa ta fuskar al'adu da yada addini da Imam Musa bin Jafar (AS) ya yi, su ne silar tsayuwar daka da dorewar mazhabar Shi'a a tsawon tarihi. Ya kara da cewa zamanin Imam Kazim (AS) lokaci ne mai tsananin gaske ga mabiya Shi'a, inda aka fuskanci jerin bore da zanga-zangar adawa da daular Abbasiyawa daga bangaren mabiya Shi'a da zuriyar Alawiyyawa.

A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza daga birnin Tehran, Hujjatul Islam wal Muslimin Ahmad Haji Abadi, yayin da yake zantawa da kamfanin, ya bayyana cewa Imam Musa Kazim (AS) ya rayu na tsawon shekaru 20 a karkashin mahaifinsa Imam Sadiƙ (AS). Ya ce: "Imam ya shaida yadda sarakuna da da ma suke nuna juyayi na munafurci ga abubuwan da suka sami Ahlul-Bait (AS), suka koma tsananta wa mahaifinsa Imam Sadiƙ (AS), wanda koyaushe yake fuskantar barazana daga Mansur (Dawaniƙiy)."

Ya ci gaba da cewa waɗannan matsin lamba sun kai matakin da ya sanya Imam ɓoye maganar imamancinsa har ga mafi yawan mabiya Shi'a, in ban da wasu tsirarun amintattu waɗanda aka umarta da su kiyaye sirri saboda leƙen asirin Mansur da mutanensa.

Zamanin Imamancin Imam Kazim (AS) Ya Yi Daidai Da Matakin Farko Na Zaluncin Abbasiyawa

A kan haka, malamin ya kara da cewa zamanin rayuwar Imam ya dace da lokacin da sarakunan Abbasiyawa suka fara nuna zalunci a bayyane. Da farko sun nuna sassauci kafin su ƙarfafa mulkinsu, amma zanga-zangar goyon bayan Alawiyyawa ya sanya sun tsorata, wanda hakan ya sa suka fara murkushe masu adawa da su. Sun kashe har da na kusa da su kamar Abdullah bin Ali Abbasiy, da Abu Salma, da Abu Muslim al-Khurasani. Sannan Mansur ya kashe Alawiyyawa da dama, wasu kuma sun rasu a gidan yari.

Imam Baƙir (AS) Da Imam Sadiƙ (AS) Sun Assasa Gagarumin Yunkuri

Malamin ya bayyana cewa wannan matsin lamba ya fara ne tun zamanin Imam Sadiƙ (AS) har zuwa zamanin Imam Rida (AS) a lokacin halifancin Ma'amun. Kafin wannan lokaci na matsin lamba, Imam Baƙir (AS) da Imam Sadiƙ (AS) sun riga sun horar da dalibai da dama wadanda suka karfafa ginin ilimi da hadisai na Shi'a, lamarin da ya haifar da gagarumin yunkuri, inda shi kuma Imam Kazim (AS) ya zo ya tsinci kansa a tsakiyar wannan matsin lamba na siyasa.

Daga nan ya bayyana cewa manufar Imam ita ce samar da daidaito na tunani a tsakanin mabiya Shi'a a lokacin da daular Abbasiyawa ta kasa amincewa da wata kungiya karkashin jagorancin Imam, wanda hakan ya sa suka tsananta masa. Imam Kazim (AS) ya karbi ragamar imamanci ne a shekara ta 148 bayan hijira bayan shahadar mahaifinsa, yayin da Mansur ya rasu a shekara ta 158 a Makka, aka rantsar da dansa Mahdi, sannan Hadi, kafin Harun al-Rashid ya karbi mulki, inda Imam ya yi shahada a shekara ta 183 bayan hijira.

Juya Hadisan Annabi Da Sarakunan Abbasawa Suka Yi

Hujjatul Islam Haji Abadi ya yi nuni da cewa, Abbasawa sun lankwasa tare da juya ma'anar shahararren hadisin Annabi (SAWA) na bayyanar mai gyara na karshe domin su daidaita shi da sunan Muhammad bin Abdullah (Nafs al-Zakiyya) ko kuma dansa Muhammad (wanda aka sani da Mahdi), domin nuna cewa shi ne ya dace da hadisin Annabi. Wannan shi ne babban karkatarwa na farko da aka yi wa wannan hadisi da duka bangarorin Shi'a da Sunna suka rawaito.

Kokarin Boye Jagoranci Shi Ne Sirrin Dorewar Shi'a

Malamin ya jaddada cewa koyarwar taƙiyya da tafiyar da al'amura a asirce da limaman Shi'a suka yi, shi ne sirrin ɗorewar mazhabar duk da tsananin ƙiyayyar da suka fuskanta. Shekaru 35 na imamancin Imam Kazim (AS) sun kasance mafi wahala saboda sun dace da zamanin sarakuna masu iko da zalunci kamar Mansur, Mahdi, Hadi, da Harun al-Rashid, inda faɗa da daular ya faɗaɗa a yankuna da dama kamar Khurasan, Iraki, da Sham.

Tonon Asirin Yaudarar Harun Al-Rashid

Daga karshe, sakataren kungiyar na gabashin Tehran ya bada misali da yadda Imam Kazim (AS) ya tona asirin yaudarar Harun al-Rashid a gaban jama'a. Yayin da Harun ya nufi kabarin Annabi (SAWA) yana cewa "Assalamu alayka ya Ibn al-Amm" (Aminci gare ka ya dan baffa na) domin nuna cewa Abbasawa sun fi kusa da Annabi fiye da kowa don halatta mulkinsu, sai Imam Kazim (AS) ya matsa gaba ya ce: "Assalamu alayka ya Ab" (Aminci gare ka ya mahaifina).

Lokacin da Harun ya nuna rashin amincewa, Imam ya yi amfani da hujjar fiƙihu inda ya ce idan Annabi ya dawo ya nemi auren 'yar Harun, zai amince? Harun ya ce kwarai da gaske. Sai Imam ya ce: "Amma ni ba zai iya auren tawa ba, domin ni jikansa ne na jini, wanda hakan ke nuna mu muka fi kusa da shi fiye da kai da kake dan baffansa."

Canjin Halayyar Dan Sindi Bin Shahak

Malamin ya kara da cewa ko da gidan yari na Sindi bin Shahak (ma'aikacin Harun) da aka tsananta wa Imam, hakan ya zama silar shiriyar da iyalansa, inda dansa Husain bin Sindi ya zama shahararren mawakin da ya rera wakoki masu yawa na yabon Ahlul-Bait (AS).

Kazalika, tsoron da daular Abbasawa take da shi ga yawan mabiya Shi'a ya sa da Imam ya rasu sakamakon guba da aka sanya masa a cikin dabino yana cikin sarka, sai da suka fito da gawar a gaban mutane 150 na gaba-gaba a Bagadaza domin su shaida cewa mutuwa ce ta dabi'a. Daga karshe, Sulaiman bin Jafar (dan Mansur) ya sayi likafani mai tsada ya binne Imam cikin girmamawa a inda ake kira Kazmain a yau, inda Imam ya kammala rayuwarsa ta jihadi.

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha